Rahotanni sun tabbatar dacewar Za a yi wa mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo tiyata a kafarsa.
Mai magana da yawunsa Laolu Akande, a cikin wata sanarwa, ya bayyana cewa tiyatar ta zama dole saboda yawan jin zafi a kafa sakamakon raunin da ya samu a lokacin da ake wasan leda.
Akande, a shafin sa na Twitter da aka tabbatar, ya ce: ''VP Osinabjo yana kwance a asibiti a yau domin yi masa tiyata saboda ciwon da ya yi a kafar da ya yi ta fama da shi a lokacin da yake wasa da wasa. Likitocinsa za su ba da bayani game da jiyya daga baya a yau.''
Leave a comment