Gwamnatin jihar Kano ta sanar da hana zirga-zirgar babura masu kafa uku da aka fi sani da A Daidata Sahu daga karfe 10:00 na dare zuwa 6:00 na safe daga ranar Alhamis 21 ga watan Yuli, 2022.

Sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai, Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa an cimma matsaya kan hakan ne a karshen taron tsaro na jihar.

Ya ce matakin wani bangare ne na kokarin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a jihar.

Kwamishinan, a cikin sanarwar, ya bukaci masu tuka baburan masu kafa uku da su bi doka su daina aiki a cikin sa’o’in da aka kayyade domin jami’an tsaro za su aiwatar da dokar ba tare da yin sulhu ba.

MALAM MUHAMMAD GARBA
Hon. Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano

Leave a comment

Quote of the week

"People ask me what I do in the winter when there's no baseball. I'll tell you what I do. I stare out the window and wait for spring."

~ Rogers Hornsby
Design a site like this with WordPress.com
Get started