Bam ya tashi a hannun ‘yan bola jari a Bama ta Jihar Borno, mutum 9 sun mutu
Rahotonni sun bayyama cewa Akalla mutane tara ne suka mutu bayan tashin wani bam a karamar hukumar Bama da ke jihar Borno.
Rundunar hadin gwiwa ta farar hula da ta bayyana hakan cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:00 na rana a jiya Litini.
Ya ce mutane tara da abin ya shafa ‘yan saran karafa ne, baban bola, wadanda ke zaune a makarantar Sakandaren ‘yan mata ta gwamnati a Bama, wanda a yanzu sansanin ‘yan gudun hijira ne.
Bama na da tazarar kilomita 68 daga Maiduguri, babban birnin jihar Borno.
Majiya Alfijir hausa
Leave a comment