Shugabar mata ta jam’iyyar APC ta kasa, Betta Edu, ta bayyana cewa Bola Ahmed Tinubu na da karfin da zai iya mayar da Najeriya babbar cibiyar tattalin arzikin duniya.
Ta yi wannan tsokaci ne a wani taro da kungiyar Mata Progressives Women Forum a Abuja, inda ta bukaci daukacin matan jam’iyyar da su fara hada-hadar goyon bayan dan takararta na shugaban kasa a 2023, Tinubu.
A cewar Edu, Tinubu ne ya fi kowa takara a zaben 2023 wanda zai iya gyara Najeriya.
Ta yi kira ga matan APC da su kunna kafafen sada zumunta na zamani don sayar da takarar Tinubu.
Leave a reply to BUBA BURGASA Cancel reply